Gwamnatin tarayya ta fara sayar da shinkafarta akan Naira 40,000

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin tarayya ta fara rabon Shinkafar da za ta sayar akan farashi mai sauki,wanda adadinta ya kai ton 30,000 .

Shirin wanda ministan noma da samar da abinci Sanata Abubakar Kyari ya kaddamar, na samar da shi ne da nufin samar da sauki ga ‘yan Najeriy sakamakon tsadar rayuwa da ake fuskanta a kansar tun bayan janye tallafin man fetur.

Za dai a rika sayar da buhunan shinkafar Mai girman 50kg a kan kudi ₦40,000.

Man Fetur shi zai rika yiwa kansa farashi yanzu a Nigeriya – NNPC

Yayin taron kaddamar da shirin a Abuja, Kyari ya jaddada cewa wannan tallafin abinci wani muhimmin bangare ne na kokarin da shugaba Bola Tinubu ke yi na ganin babu wani dan Najeriya da ya kwana da yunwa. Shirin wanda aka tsara shi da gaskiya, za a raba shinkafa a duk fadin kasar, inda ake bukatar masu saye su gabatar da Lambar Shaidar katin dan Kasa (NIN) da lambobin wayarsu domin tantancewa.

 

“Wannan shiri ya zo kan lokacin da ya dace, duba da irin kalubalen da muke fuskanta a kasa baki daya,” in ji Kyari, yana mai cewa shirin sayar da shinkafar har miliyan 30,000 ana sa ran zai taimaka wajen daidaita farashin shinkafa da sauran kayan abinci.

Yanzu-yanzu:Kotu ta baiwa hukumar zaben Kano umarni Kan zaben kananan hukumomi

Ya ce za a sanya idanu sosai a raba shinkafar don tabbatar da cewa wadanda aka yi tsarin don su sun amfana musamman mutane masu karamin karfi da ma’aikatan gwamnati.

Domin tabbatar da gudanar da rabon Shinkafar cikin kwanciyar hankali, gwamnati ta samar da wuraren sayar da ita da dama a fadin babban birnin tarayya da sauran jihohi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...