Gwamnatin tarayya ta fara sayar da shinkafarta akan Naira 40,000

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin tarayya ta fara rabon Shinkafar da za ta sayar akan farashi mai sauki,wanda adadinta ya kai ton 30,000 .

Shirin wanda ministan noma da samar da abinci Sanata Abubakar Kyari ya kaddamar, na samar da shi ne da nufin samar da sauki ga ‘yan Najeriy sakamakon tsadar rayuwa da ake fuskanta a kansar tun bayan janye tallafin man fetur.

Za dai a rika sayar da buhunan shinkafar Mai girman 50kg a kan kudi ₦40,000.

Man Fetur shi zai rika yiwa kansa farashi yanzu a Nigeriya – NNPC

Yayin taron kaddamar da shirin a Abuja, Kyari ya jaddada cewa wannan tallafin abinci wani muhimmin bangare ne na kokarin da shugaba Bola Tinubu ke yi na ganin babu wani dan Najeriya da ya kwana da yunwa. Shirin wanda aka tsara shi da gaskiya, za a raba shinkafa a duk fadin kasar, inda ake bukatar masu saye su gabatar da Lambar Shaidar katin dan Kasa (NIN) da lambobin wayarsu domin tantancewa.

 

“Wannan shiri ya zo kan lokacin da ya dace, duba da irin kalubalen da muke fuskanta a kasa baki daya,” in ji Kyari, yana mai cewa shirin sayar da shinkafar har miliyan 30,000 ana sa ran zai taimaka wajen daidaita farashin shinkafa da sauran kayan abinci.

Yanzu-yanzu:Kotu ta baiwa hukumar zaben Kano umarni Kan zaben kananan hukumomi

Ya ce za a sanya idanu sosai a raba shinkafar don tabbatar da cewa wadanda aka yi tsarin don su sun amfana musamman mutane masu karamin karfi da ma’aikatan gwamnati.

Domin tabbatar da gudanar da rabon Shinkafar cikin kwanciyar hankali, gwamnati ta samar da wuraren sayar da ita da dama a fadin babban birnin tarayya da sauran jihohi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...