Da dumi-dumi: Tinubu zai tafi ƙasar Equatorial Guinea

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Shugaban kasa Bola Tinubu zai tashi daga Abuja zuwa birnin Malabo na kasar Equatorial Guinea a ranar laraba 14 ga watan Agusta a wata ziyarar aiki ta kwanaki uku

Tinubu zai je kasar ne domin girmama gayyatar da shugaba Teodoro Obiang Nguema Mbasogo ya yi masa.

Dalilin da ya haifar da rikici tsakanin yan bindiga har suka kashe 30 daga cikinsu

Tinubu, a cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale, ya fitar, zai gana da shugaban kasar Equatorial Guinea a fadar shugaban kasar idan ya da isa, inda za a yi taruka tsakanin shugabannin biyu da kuma kulla yarjejeniyoyin da suka shafi man fetur da iskar gas da kuma tsaro.

Zargin karkatar da shinkafa: EFCC ta karɓi korafi kan shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin Kano

Shugaban Najeriyar dai zai samu rakiyar ministan harkokin wajen kasar Ambasada Yusuf Tuggar da sauran mukarraban gwamnatinsa, wadanda za su sa hannu wajen rattaba hannu kan yarjejeniyoyin da kuma nazarin damarmakin inganta alakar da ke tsakanin kasashen biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...