Da dumi-dumi: Buhari, Jonathan da wasu shugabanni sun gana da Tinubu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

 

Shugaba Bola Tinubu yanzu haka na jagorantar taron majalisar kasa, wadda ta kunshin tsofaffin shugabannin Nigeria a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Taron wanda shi ne irinsa na farko a tun bayan rantsar da shugaba Tinubu a ranar 29 ga watan Mayun 2023, taron yana gudana ne a zauren majalisar tare da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.

Taron wanda aka fara da karfe 12:27 ya sami halartar taron tsoffin shugabannin kasa, Janar Abdulsalam Abubakar da Yakubu Gowon ta na’urar gani ga ka.

Zargin karkatar da shinkafa: EFCC ta karɓi korafi kan shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin Kano

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo da tsohon shugaban kasa Ibrahim Babangida ba su halarci taron ba.

Wadanda suka halarci taron sun hada da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima, shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio; Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike da wasu Gwamnonin Jihohi da Mataimakan Gwamnoni.

Taron farkon dai ana sa ran zai tattauna halin da al’ummar kasar ke ciki musamman kalubalen tattalin arziki da al’ummar kasar ke fuskanta.

Da dumi-dumi: Gwamnatin Kaduna ta janye dokar hana fita

Majalisar wadda kundin tsarin mulkin Tarayyar Najeriya na 1999 ya amince da ita, tana taka muhimmiyar rawa wajen bayar da shawarwari a cikin harkokin mulkin kasa.

Majalisar wadda ta kunshi shugaban kasa a matsayin shugaba da mataimakin shugaban kasa a matsayin mataimakin shugaban majalisar, ta kuma kunshi dukkanin tsofaffin shugabannin kasa da shugabannin kasa, da dukkan tsofaffin alkalan Najeriya, shugaban majalisar dattawa, kakakin majalisar wakilai, gwamnonin jihohi da lauyoyi da Janar- janar na kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...