Yadda Jaruma Rahama Sadau ta raba Naira Miliyan 1 ga Masoyanta

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

Shahararriyar jarumar nan Rahama Sadau da ta yi fice a fina-finan duniya ta rabawa mabiya shafinta na Facebook zunzuruntun kudi har Naira Miliyan 1.

Jarumar dai ajiya ta wallafa cewa za ta raba kudi ga wasu mutane 100 wanda za ta zaba kai tsaye da kanta inda wasu har suna ganin lamarin wasa ne kwatsam sai akaji saukar dubu 10, 10 ga mutanen da suka aje lambar Asusun Bankinsu.

Talla
Talla

Sadau Yar Najeria ce Wadda ta Fara Fim Daga Masana’antar Kannywood har takai kololuwar mataki a fannin fina-finan Duniya Inda ba iya Najeria ba har kasashen ketare na Alfahari da ita.

Idan zanga-zanga ta ƙazance to fa za mu ɗau mataki — Sojoji

Wani abun ban sha’awa na Jarumar Shi ne Yadda Babu girman kai a tare da ita take iya bibiyar mabiyan nata ta yi musu like ko Comment wani Zubin Dama Sharing Abinda suka rubuta hakan yasa wata shakuwa tsakaninta da Mabiyanta a yanzu da sabuwar soyayya.

Rahama dai ta sake dawowa a fagen shuhura inda da dama suke alakanta girmama mutane da Ra’ayinta da Ilimin da take dashi bata duba daukaka, dubun dubatar mutane suna kara nuna soyayyarsu agareta inda har yanzu Soyayyar ke nuna cewa Acikin Mata Masu Fina Finai Babu Kamarta.

Mutanen da suka sami kyautar kudin sun bayyana Jin dadinsu, inda suke cewa Jarumar ta tallafa musu a daidai lokacin da suke bukata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...