Idan zanga-zanga ta ƙazance to fa za mu ɗau mataki — Sojoji

Date:

Babban Hafsan Tsaro (CDS), Christopher Musa, ya ce sojoji za su shigo ciki idan zanga-zangar ‘#EndbadGovernance’ da ke ci gaba da gudana a fadin kasar ta ci gaba da rikide wa zuwa tashin hankali.

Musa dai na mayar da martani ne kan barna da sace-sace da aka yi a zanga-zangar da aka yi a sassa da dama na kasar a ranar Alhamis.

Talla
Talla

Ko a ranar ma sai da aka farfasa cibiyar sadarwa ta musamman ta NCC a Kano, inda aka sace kayaiyaki na biliyoyin Naira.

Da yake zantawa da manema labarai a jiya Juma’a, Musa ya bukaci masu zanga-zangar da su gane cewa barna ba ta da amfani kuma zai jefa al’ummar kasar cikin rudani.

Atiku ya jinjinawa masu zanga-zanga, ya bukaci Tinubu ya saurari koken jama’a

Yayin da yake yabawa rundunar ƴansandan Najeriya bisa kokarin da take yi na tabbatar da zaman lafiya, ya kara da cewa za a tilastawa sojoji shiga lamarin idan har aka ci gaba da samun tashin hankali.

Ya ce: “Ya kamata mu gane cewa wadannan barna da kudaden mu aka samar da su kuma da kudaden mu za a gyara su idan kuka bata.

“Don haka maimakon yin haka, ya kamata mu hada kai don tabbatar da cewa babu wani abu. ya lalace,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...