Zanga-zanga: Yadda Mu ka gano makarkashiyar ’yan siyasa na haddasa fitina a Kano – Gwamna Yusuf

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya koka kan yadda wasu ‘yan siyasa da bai bayyana sunayensu ba ke shirin haifar da tsarzoma a ranar 1 ga watan Agusta a jihar.

Yusuf, wanda ya bayyana hakan a ranar Laraba, ya ce gwamnatinsa ta bankado wani yunkuri da wasu ‘yan siyasa marasa kishi suke yi na fakewa da sunan zanga-zangar domin tayar da tarzoma.

“A shirye muke mu karbi masu zanga-zangar lumana a gidan gwamnati. Ba zan gudu ba, su kawo kokensu zan kaiwa Shugaba Tinubu, mu gabatar masa da matsayinmu,” inji Gwamnan.

Talla
Talla

Ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta sake duba farashin man fetur da wutar lantarki tare da bude iyakokin kasar domin ba da damar shigo da kayayyaki cikin kasar nan.

Yusuf ya kuma bukaci gwamnati da ta rage tsadar kayayyakin masarufi domin saukakawa ‘yan Najeriya.

Karin bayani kan jadawalin zaɓen kananan hukumomi na Kano

“Bari in tuna muku, lokacin da muka hau mulki sai da muka yi iya bakin kokarinmu don tabbatar da dawo da zaman lafiya jihar.

Mun gano wani yunkuri da wasu ‘yan ‘yan siyasa suka yi na sayen jar hula da raba su ga ‘yan daba da za su yi amfani da su a yayin zanga-zangar don yin sace-sace a shaguna mutane wadanda ba su ji ba ba su gani ba,” inji shi.

Gwamnan ya ce gwamnatinsa na shirin samar da ofishin da zai rika kula da farashin kayayyaki a jihar domin tabbatar da an daidaita farashin da kayiyyaki.

Talla

Ya ce gwamnatinsa ta dukufa wajen ganin cewa rayuwa ta zama mai sauki ga talaka, ya kara da cewa gwamnati ta dawo da akwatunan karbar shawarwarin jama’a domin karbar shawarwari kai tsaye daga jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...