Za mu duba tare da bayar da magunguna kyauta ga marasa lafiya a karamar hukumar Wudil – Bilkisu Indabo

Date:

Daga Samira Ahmad

 

Shugabar riko ta karamar hukumar wudil Hajiya Bilkisu Yakubu Indabo ta ce zata hada gwiwa da hukumar masu yiwa kasa hidima wajen ba da magunguna kyauta da al’ummar karamar hukumar.

“Cikin wata yarjejeniyar haɗin gwuiwa da mukayi tsakanin Ƙaramar Hukumar Wudil da reshen ɗalibai masu bautawa ƙasa (NYSC) na Wudil, zamu gudanar da wata shirin dubawa da rabon magungunnan cututtuka irin su hawan jini, zazzaɓin typhoid da shauran nau’ikan gama garin cututtuka”.

Talla
Talla

Hajiya Bilkisu Indabo ta bayyana hakan ne yayin wata ganawa da jaridar kadaura24.

“In sha Allahu nan da ƴan kwanaki kaɗan zamu sanar da ranar da zamu gudanar da wannan taro domin al’ummar Ƙaramar Hukumar Wudil su fito su amfana”. Inji Shugabar

Rarara ya Magantu AKan Goge Shafinsa da Facebook Ya Yi

Ta ce da ma bannin kula da lafiyar al’umma na daga cikin manyan abubunwan da ta fi baiwa muhimmanci, ta kuma yi alkawarin cigaba da Kula da lafiya da Ilimi a karamar hukumar .

“Kamar yadda aka sani, a matsayi na ta ma’aikaciyar lafiya kuma malamar ilimi, zan cigaba da bayarda da fifiko a wannan ɓangare dama shauran ɓangarori masu amfani kai tsaye ga al’umma ta domin bauta musu yadda ya dace”. A cewar Bilkisu Indabo

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...