Za mu duba tare da bayar da magunguna kyauta ga marasa lafiya a karamar hukumar Wudil – Bilkisu Indabo

Date:

Daga Samira Ahmad

 

Shugabar riko ta karamar hukumar wudil Hajiya Bilkisu Yakubu Indabo ta ce zata hada gwiwa da hukumar masu yiwa kasa hidima wajen ba da magunguna kyauta da al’ummar karamar hukumar.

“Cikin wata yarjejeniyar haɗin gwuiwa da mukayi tsakanin Ƙaramar Hukumar Wudil da reshen ɗalibai masu bautawa ƙasa (NYSC) na Wudil, zamu gudanar da wata shirin dubawa da rabon magungunnan cututtuka irin su hawan jini, zazzaɓin typhoid da shauran nau’ikan gama garin cututtuka”.

Talla
Talla

Hajiya Bilkisu Indabo ta bayyana hakan ne yayin wata ganawa da jaridar kadaura24.

“In sha Allahu nan da ƴan kwanaki kaɗan zamu sanar da ranar da zamu gudanar da wannan taro domin al’ummar Ƙaramar Hukumar Wudil su fito su amfana”. Inji Shugabar

Rarara ya Magantu AKan Goge Shafinsa da Facebook Ya Yi

Ta ce da ma bannin kula da lafiyar al’umma na daga cikin manyan abubunwan da ta fi baiwa muhimmanci, ta kuma yi alkawarin cigaba da Kula da lafiya da Ilimi a karamar hukumar .

“Kamar yadda aka sani, a matsayi na ta ma’aikaciyar lafiya kuma malamar ilimi, zan cigaba da bayarda da fifiko a wannan ɓangare dama shauran ɓangarori masu amfani kai tsaye ga al’umma ta domin bauta musu yadda ya dace”. A cewar Bilkisu Indabo

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...