Iftila’i: Gobara ta hallaka ‘yar Kwamishina a Kano, da yan uwansa biyu

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

Gobara ta yi sanadiyar hallaka yar Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar Kano, Yusuf Kofar-Mata, tare da wasu yan uwansa guda biyu.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a shafin sa na Facebook a ranar Laraba.

Marigayiyar dai ‘yarsa ce mai suna Maimuna, sai yayarsa, Khadija, da matar dan uwansa, Juwairiyya.

Talla

Rahotanni sun bayyana cewa gobara ta kone gidan kwamishinan da ke Kofar-Mata a birnin Kano da safiyar Laraba yayin da iyalan ke barci.

Wata majiyar daga cikin danginsa ta ce gobarar ta lalata wasu kayayyaki masu daraja a gidan.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya soki gwamnatin Kano kan sabbin masarautu masu daraja ta biyu

Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar, Abdullahi Saminu, ya ce har ba a iya gano adadin barnar da gobarar ta yi ba, da kuma musabbabin tashin gobarar.

A halin da ake ciki, Kofar-Mata ya bayyana alhininsa game da rasuwar yar tasa da wasu ’yan uwansa guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda Shugabanni da jagororin Jam’iyyar APC na Kano suka kauracewa tarbar Kashim Shattima yayi ziyarar ta’aziyya

Daga Fatima Mahmoud Diso   Shugabanni da jagororin jam'iyyar APC na...

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...

Damuna: Mun shirya inganta wuraren tsayarwar motocinmu – Kungiyoyin Direbobin na Kano

Kungiyar matuka motocin kurkura ta jihar Kano da Kungiyar...

Rasuwar Aminu Ɗantata babban rashi ne ba ga Nigeria kadai ba – Mustapha Bakwana

Daga Zakaria Adam Jigirya   Tsohon Mai baiwa gwamnan Kano shawarawa...