Iftila’i: Gobara ta hallaka ‘yar Kwamishina a Kano, da yan uwansa biyu

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

Gobara ta yi sanadiyar hallaka yar Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar Kano, Yusuf Kofar-Mata, tare da wasu yan uwansa guda biyu.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a shafin sa na Facebook a ranar Laraba.

Marigayiyar dai ‘yarsa ce mai suna Maimuna, sai yayarsa, Khadija, da matar dan uwansa, Juwairiyya.

Talla

Rahotanni sun bayyana cewa gobara ta kone gidan kwamishinan da ke Kofar-Mata a birnin Kano da safiyar Laraba yayin da iyalan ke barci.

Wata majiyar daga cikin danginsa ta ce gobarar ta lalata wasu kayayyaki masu daraja a gidan.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya soki gwamnatin Kano kan sabbin masarautu masu daraja ta biyu

Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar, Abdullahi Saminu, ya ce har ba a iya gano adadin barnar da gobarar ta yi ba, da kuma musabbabin tashin gobarar.

A halin da ake ciki, Kofar-Mata ya bayyana alhininsa game da rasuwar yar tasa da wasu ’yan uwansa guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...