An Sako Mahaifiyar Mawaki Rarara Da Aka Sace

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Mahaifiyar fitaccen mawakin siyasar nan Dauda Kahutu Rarara Hajiya Hauwa’u Adamu, ta sami ‘yanci bayan shafe kwanaki 20 a hannun masu garkuwa da mutane.

Rarara ne ya tabbatar da labarin kubutar mahaifiyar tasa a sahihin shafinsa na shafin sa na Instagram a safiyar Larabar nan.

Talla

Duk da har yanzu babu cikakken bayanin yadda aka sako dattijuwar mai kimanin mai shekaru 75, amma rahotannin da ba a tabbatar da su ba sun ce an biya wasu makudan kudade a matsayin kudin fansa kafin a Sako dattijuwar.

Gwamnan Kano ya nada sabbin Sarakuna 3 masu daraja ta biyu

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito an sace mahaifiyar mawaki Rarara ne a jihar Katsina a cikin watan da ya gabata.

A halin da ake ciki kuma, rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a baya ta sanar da kama wasu mutane biyu da ake zargi da hannu wajen yin garkuwa da su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...