Rashin katabus: Gwamnatin Kano ta baiwa Pillars wa’adin wasanni uku na su farfaɗo da ƙoƙarin su

Date:

 

Gwamnatin jihar Kano ta bayar da wa’adin wasanni uku ga mahukuntan kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars domin dawo da ƙoƙarin ta da samun nasara a jere.

Mukaddashin Kwamishinan Matasa da Wasanni, Hamza Safiyanu Kachako ne ya ba da wa’adin, biyo bayan rashin kokari da kungiyar ke yi a kwanakin nan a gasar Firimiyar Najeriya ta kakar 2023/24.

Kano Pillars, wadda aka fi sani da “Sai Masu Gida,” ta fuskanci koma baya a wasanni na baya-bayan nan, inda ta sha kashi a hannun Bendel Insurance na Benin da ci 2-1. Kafin rashin nasarar kungiyar ta sha fama da rashin nasara a jere da suka hada da rashin nasara a hannun Shooting Stars da ci 1-2 da kuma rashin nasara da Enyimba International da ci 5-0.

Ya Kamata Gwamnati ta Fara Tilastawa Yan Kasuwa Don su Sauke Farashin Kayan su – Falakin Shinkafi

Sai dai Kwamishinan ya jaddada kudirin gwamnatin jihar, karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf na taimakawa Kano Pillars baya domin samun nasara.

Gwamnan Kano ya chanzawa wasu daga cikin Kwamishinonin sa ma’aikatu

Sai dai ya bayyana cewa dole ne a dauki kwararan matakai don dawo da kungiyar zuwa ga nasara, inda ya bayyana cewa gwamnati ba za ta sa ido kan yadda ƙungiyar ta Kano ke tabarbare wa ba.

Daga nan ne aka bukaci mahukunta da ma’aikatan kungiyar ta Kano Pillars da su sauya al’amura a wasanni uku masu muhimmanci da za su fara da wasan da za su kara da kungiyar Gombe United a ranar Lahadi, 21 ga Afrilu, 2024, a filin wasa na Sani Abacha, Kano.

Za a kuma ta buga wasa a waje da Akwa United da kuma karawar gida da Doma United ta Gombe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...