Ya Kamata Gwamnati ta Fara Tilastawa Yan Kasuwa Don su Sauke Farashin Kayan su – Falakin Shinkafi

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Falakin Shinkafi Amb. Yunusa Yusuf Hamza, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi da su yi kira ga Yan kasuwa domin su sauke farashin kayayyakin su ko kuma su dauki matakan da suka dace akan su.

“Al’umma suna cikin wani hali tun lokacin da Dala ta tashi, mussaman yadda farashin kayan Masarufi sukai tashin gauron zabi a fadin Najeriya”.

Amb. Yunusa Yusuf ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi wakilin Kadaura24 a Kano.

An janye ‘yan sandan da ke gadin tsohon gwamnan Kogi Yahaya Bello

“Talaka ya shiga wani hali na matsin rayuwa saboda yadda ake maganar Dala tayi tashin gauron zabi, sai gashi kuma yanzu Dala ta sauko, to shin mai ya kamata Yan kasuwar mu suyi a yanzu? Shi ne su sauke farashin kaya domin Talaka ya samu sauki”. Falakin Shinkafi

Yace duk dan kasuwar da zai yi ikirarin cewar Dala ta tashi zai kara kudin kaya, to ya kamata tunda yanzu Dala ta sauko ya sauke farashin kayansa idan har da gaske yake.

Gwamnan Kano ya chanzawa wasu daga cikin Kwamishinonin sa ma’aikatu

“Muna kira ga gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusif yadda ya zauna da Yan kasuwa a baya, da yanzu ma ya taimaka ya zauna da su domin talakawa su samu saukin halin da suke ciki”. A cewar Falakin Shinkafi

Hatta gwamnatin tarayya muna kira gare ta da tayi abinda ya dace akan Yan kasuwar mu, domin tabbatar da cewa sun sauke farashin kayansu.

A cewar Falakin Shinkafi “A lokacin da Dala ta kusa kaiwa 2000, Dan kasuwa zai siyo abu a naira 200 sakamakon tashin Dala, to a yanzu Dala ta sauko tana 1050 kuma yan kasuwa suna siyar da kaya akan Naira 195, wanda hakan bai kamata ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...