APCn Kano ta yi Martani Kan dakatar da aka yiwa Ganduje

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Jam’iyyar APC reshen jihar Kano, ta dau tsauraran matakai kan wasu jiga-jigan jam’iyyar na mazabar Ganduje da suka ce sun dakatar da shugaban jam’iyyar na kasa Umar Abdullahi Ganduje.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito jam’iyyar APC ta mazabar Ganduje da ke karamar hukumar Dawakin Tofa ta dakatar da Ganduje.

Shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Dawakin Tofa, Inusa Dawanau, ya shaida wa manema labarai cewa, wadanda suka dakatar da shugaban jam’iyyar na kasa abun da suka yi ya sabawa doka, kuma suna zargin yan adawa ne suka kitsa lamarin .

Yanzu-Yanzu: APC ta Dakatar da Ganduje Daga Jam’iyyar

Yace kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na jihar ya ce sun dakatar da wadanda suka ce sun dakatar da Ganduje har na tsahon watanni 6, sannan kuma an kafa kwamitin bincike na musamman domin tabbatar da wasu zarge-zarge da ake yi musu.

Shugaban Jam’iyyar na Kano, Abdullahi Abbas, ya ce sun amince da shawarar da shugabannin Jam’iyyar suka dauka.

Ali Nuhu, Ali Jita, Abale da Wasu Yan Kannywood syun Yiwa Adam A Zango Martani

“Muna da hujjojin da zasu tabbatar da ganawar da wadancan mutane suka yi da jami’an gwamnatin jihar kano. Kwamitin ayyuka na jihar ya amince da sanya musu takunkumi na tsawon watanni shida, kuma yanzu haka sun dakatar da su.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...