Murtala Sule Garo Ya Yiwa Al’ummar Kano Barka da Sallah

Date:

 

Tsohon dan kararar mataimakin gwamna a jam’iyyar APC a Jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo na yiwa daukacin al’ummar musulmi barka da sallah.

Kadaura24 ta rawaito a wani sakon taya murna Alhaji Murtala Sule Garo ya ce bikin Sallar bai takaita ba ne kawai ga kammala azumin wajibi na watan ramalana, ya hada da fadakar da tunatard al’umma don ganin an samu zaman lafiya da arziki mai daurewa a JIhar Kano da Kasa baki daya.

Yanzu-yanzu: CBN Ya Sake Karya Farashin Dala a Nigeria

Sule Garo ya ce, “Ina taya daukacin al’ummar musulmi musamman na jihar Kano barka da sallah.

“Muna godiya ga Allah madaukakin sarki da ya bamu ikon azumtar watan ramalana. Allah ya karbi ibadinmu, ya yafe mana kurakuranmu, ya kuma kara aramana lokaci nan gaba.

“Ina kira ga al’umma musulmi da su yi amfani da darusan da muka koya cikin wannan wata mai alfarma dan tabbatar da zama lafiya da kaunar juna a jiharmu da kuma kasa baki daya.

Tabbas ‘yan najeriya na cikin wani mawuyacin hali sakamakon tabarbare tattalin arziki. Amma duk da haka ba ma cire kauna ga kasarmu ba. Dan haka wannan lokaci wata dama ce a garemu da za mu ci gaba da addu’o’i Allah ya kawo mana mafita da arziki mai daurewa.”

Barka da Sallah

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Za mu kashe Sama da Naira miliyan 105. Dan Bunkasa Harkar ilimi a karamar hukumar Dala – Hon Surajo Imam

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Surajo...

Zaben 2027: Kwankwaso ya bugi kirji

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano, ya...

Sha’aban Sharada ya sami sabon mukami

Daga Sharifiya Abubakar   Kungiyar ‘yan majalisun dake kula da tsaro...

Dan Majalisar NNPP ya fice daga jam’iyyar zuwa APC

  Yusuf Galambi dan majalisar wakilai ya sauya sheka daga...