Abubuwan da ya Kamata ku sani game da Jaruma Saratu Gidado Daso

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

An haifi Saratu Gidado wadda akafi sani da Daso a ranar 17 ga watan janairu na shekara ta 1968 a jihar Gombe dake arewa maso gabshin Nigeria.

Saratu Gidado ta yi karatunta na firamare a chiranchi dake karamar hukumar Gawle a jihar kano ta kano, kuma ta shiga masana’antar kannywood a s shekara ta 2000.

ta bayar da gudunmwa a fina-finai da dama da daga cikin su akwai: Linzami da wuta, Mashi, Fil’azal, Jaridar, Garwashi, Mu rike amana,, Sakace, Takun saka, Sammatsi, Bakar tukunya, Gabas, Lamba, Yayan baiwa, Sabon shafi da dai sauransu.

Yanzu-yanzu: Allah ya yiwa Jarumar kannywood Daso Rasuwa

Hajiya Saratu Gidado tana daga cikin Jakadun Sarkin Kano tun lokacin sarkin Kano na 14 Muhammadu Sanusi II har zuwa Sarkin kano na yanzu Alhaji Aminu Ado Bayero.

Saratu Gidado tana gaishe da sarkin Kano

Ka Yi Aikin Dake Gabanka Ka Rabu Da Ganduje – Kwankwaso Ya Fadawa Abba Gida-gida

Marigayiyar ta kuma shahara wajen nemawa marasa karfi da Marayu taimako musamman a shafukan sada zumunta.

Hajiya saratu Gidado wadda ta Shahara a masana’antar Kannywood ta rasu ne ba tare da wata rashin lafiya ba kamar yadda Shugaban kungiyar jaruman Kannywood Alhsan kwalli ya Shidawa manema labarai.

Tuni dai an yi jana’izar ta kamar yadda Addinin Musulunci yayi tanadi, kuma mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ne ya jagoranci jana’izar ta ta a fadar sarkin dake kofar kudu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...