Malam Daurawa ya bayyana sunayen wadanda suka Sulhunta su da Gwamnan Kano

Date:

Daga Rabi’atu Yunusa Adam

 

Kwamandan Hukumar Hisbah ta jihar kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya mika godiya ga wasu muhimman mutane da yake sun taka rawa wajen sulhunta su da gwamnan Kano bisa abun da ya faru a tsakanin su.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito Malam Aminu Daurawa ya ajiye mukamin sa ne bayan da gwamna Abba Kabir Yusuf ya kalubalanta yadda hukumar take gudanar da aikin kamo mata masu aikata bidala a jihar.

Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana haka ne Lokacin da ya ke komawa Ofishinsa Na Shugaban hukumar Hisba a ranar Talata.

Gwamnan Kano ya Turawa Majalisar Dokoki Sunayen Kantomomi 44 Domin Tantancewa

“Ina godiya da mai alfarma sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III wanda da kansa ya kirawo ta waya akan batun, sai Alhaji Dahiru Mangal Wanda shi kuma har zazzabi ma yayi saboda abun da ya faru, shi kuwa Farfesa Ibrahim Maqari Babban Limamin masallacin kasa tun daga Abuja ta taso ya zo Kano saboda abun da ya faru “.

Bidiyon Dala: Kotu ta Yanke Hukunci Kan Karar da Ganduje Ya Kai Hukumar Yaki da Cin Hanci ta Kano

Malam Daurawa ya kara da cewa dole ya godewa Sheikh Ali Isa Fantami Wanda shi kuma Kwankwaso ya Samu ya yiwa magana akan batun, shi kuma Kwankwaso matsayinsa na jagora ya kirawo ni a waya muka tattauna akan batun. Don haka dole Ina godewa wadannan mutane da ma wadanda ban sami damar ambatar sunansu ba, musamman Inuwar hadin kan malaman jihar kano da sauran su.

Sheikh Daurawa ya kuma bayyana shirin hukumar ta Hisba na ci gaba da gudanar da ayyukansu domin tsaftace ayyukan badala a jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...