Tinubu ta gargaɗi Kungiyar Kwadago kan zanga-zangar da ta shirya yi a Nigeria

Date:

Gwamnatin Najeriya ta yi kira ga ƙungiyar ƙwadago ta ƙasar NLC da ta jingine zanga-zangar da ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar ranakun 27 da 28 ga wannan wata, kan tsadar rayuwa.

Ministan Shari’a na ƙasar, Lateef Fagbemi, SAN ne ya bayyana gargaɗin cikin wata wasƙa da ya aike wa lauyan ƙungiyar ƙwadagon, Femi Falana ranar Juma’a.

Yanzu-yanzu: ECOWAS ta dage takunkumin da ta kakaba wa Nijar, Mali, Guine

Ministan ya ce “Gwamnati na ƙoƙarin kammala duka batutuwan da ta cimma da ƙungiyar, kuma abin da ya kamata shi ne NLC ta tuntuɓi gwamnati don tabbatar da aiwatar da yarjejeniyoyin da aka cimma, musamman a ɓangarorin da matsaloli suka yi katutu”.

Ya ƙara da cewa zanga-zangar da ƙungiyar ta shirya gudanarwa ta ci karo da umarnin da kotun da ke hukunta laifukan da suka shafi gwamnati da ƙungiyar ƙwadago.

Kamata yayi Gwamnati ta cirewa kayan masarufi haraji ta mai dashi kan Giya, sigari da kayan kyalekyale – Falakin Shinkafi

Ministan ya ce ƙungiyar ta shirya gudanar da zanga-zangar ne saboda zargin gwamnati ta kasa aiwatar da batutuwan da ta cimma da ƙungiyar ƙwadagon ranar 2 ga watan Oktoban bara.

A cikin wasikar ministan ya buƙaci lauyan ƙungiyar ya bai wa ƙungiyar shawarar datakar da zanga-zangar wanda ya ce za ta iya dakatar da ayyukan gwamnati da barazana ga zaman lafiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...