Gwamnatin Tarayya ta Bayyana Dalilin da Yasa ta Rufe Kantin Sahad Store

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Hukumar Kare Hakkin Mai Saye Ta Gwamnatin Tarayya (FCCPC), ta rufe katafaren shagon sayar da kayayyaki na Sahad Store da ke Abuja, kan zargin su da kara wa kwastomomi farashin kaya.

Jami’an hukumar da ke kare hakkin masu saye ne suka rufe, babban shagon nan na Sahad Stores da ke yankin Area 11 a Abuja.

Wannan na zuwa ne bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana hanyoyin dakile matsalar karancin abinci da tsadarsa a fadin Najeriya.

Kotu A Kano Ta Yanke Wa Mutumin Da Aka Kama Da Murja Kunya Hukunci

An dai zargin cewa masu katafaren shagon da kara wa kwastomomi kudin kaya fiye da farashin da ke makale a jikin kayan.

Shugaban hukumar, Adamu Ahmed Abdullahi ya ce wani bincike da hukumar ta gudanar kan katafaren shagon ya nuna yadda suke cutar mutane.

Ya kara da cewa shagon zai ci gaba da kasancewa a rufe har zuwa lokacin da za a kammala bincike.

Da dumi-dumi: Hukumar Hisbah ta sake kama wata yar TIKTOK a Kano

“Mun fahimci cewa mutanen nan abin da suke yi yaudara ne, inda babu gaskiya dangane da farashin kayan da suke sayarwa wanda kuma hakan ya yi karo da sashe na (135) da dokar da ta hana a yaudarar abokin hulda.”

Wannan dai na zuwa ne bayan da ‘yan Najeriya ke ci gaba da kokawa kan yadda farashin kayayyaki ke tashin gwauron zabi.

Hakan ne ya sanya Shugaba Tinubu gana wa da gwamnonin jihohi a ranar Alhamis , don tattauna hanyar da za a dakile tashin farashin kayayyaki da kuma magance matsalar tsaro.

Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar almajirai da yaran da ba sa zuwa Makaranta ta kaddamar da yi wa yaran da ba sa zuwa Makaranta Rijista a Kano

Daga Saminu Ibrahim Magashi   Hukumar kula da almajirai da yaran...

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban ƙasa – Barau Jibrin

Daga Isa Ahmad Getso Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata...

Inganta tsaro: Shugaban K/H Tarauni ya ba da fili domin gina ofishin Civil Defence a karkasara

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Shugaban karamar hukumar Tarauni, Alhaji Ahmed...

Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nada Malam...