Gwamnatin Kano ta bada hutun sabuwar shekarar Musulunci

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana gobe Alhamis, 26 ga Yuni, 2025, a matsayin hutu domin shiga Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447 Hijira.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kuma taya al’ummar Musulmi murna bisa samun damar ganin sabuwar shekarar, wadda ke farawa da watan Muharram – watan farko a kalandar Musulunci ta hijira.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya aikowa Kadaura24 a yau Laraba.

InShot 20250309 102512486
Talla

Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da kuma Musulmi gaba ɗaya da su yi duba kan ayyukansu na shekarar da ta gabata, tare da amfani da wannan dama domin yin addu’o’i na zaman lafiya, haɗin kai da cigaba a jihar da kuma ƙasa baki ɗaya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...