‘Yan Sandan Kano Sun Kama Wasu ‘Yan Daba da akai hayarsu Don Tada Tarzoma a Wajen Zabe

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da cafke wasu ‘yan daba da ake zargin an dauko hayar su domin kawo cikas a zaben da aka gudanar a karamar hukumar Kunchi a jihar.

Usaini Gumel, kwamishinan ‘yan sandan jihar ne ya sanar da hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a ranar Asabar.

Yanzu-yanzu INEC ta Bayyana Dalilan ta na Dkatar da Zaɓen Kunchin da tsanyawa

Gumel wanda bai bayyana adadin mutanen da aka kama ba ya ce yan dabar an kama su ne dauke da da aka makamai.

Ya ce wadanda ake zargin wani dan siyasa ne da ke takara a zaben ya dauki hayar su.

“Mun ga wata babbar mota dauke da mutane gefen hanya. Da farko mun zaci man fetur din motar ne ya kare. Amma muka je kusa dasu sai muka gansu da makamai.

Zaben Cike Gurbi: INEC ta Magantu Kan Sace Akwatunan Zabe a Kano

“Wani Abdulrazaq Muhammad wanda aka fi sani da Mai Salati daga karamar hukumar birnin Kano ya shaida mana cewa wani mutum da ya ke takara a yankin ya gayyace su.

“Za mu tuntubi mutumin domin tabbatar da cewa ko yana cikin yan takarar da kuma dalilin da ya sa ya gayyace su yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...