Yan sanda sun kama likitan bogi dake zubar da ciki a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kano ta ce ta kama wani matashi mai shekara 19 da zargin yi wa ‘yar uwarsa ciki a ƙaramar hukumar Tofa da kuma zargin haɗa baki wajen kashe ta.

Wata sanarwa da Kakakin rundunar SP Abdullahi Kiyawa ya aikowa kadaura24, ta ce runundar ta ce ta kama Ukasha Muhammed ne bayan ta samu rahoton cewa ya yi wa Amina Bala mai shekara 19 ciki, sannan ya kai ta wajen wani mai suna Chidera Ugwu don ya yi mata allurar zubar da cikin.

Talla

Sanarwar ta ce Mista Ugwu, wanda likitan boge ne, ya yi mata allura tare da ba ta wasu ƙwayoyin magani da zimmar zubar da cikin, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarta.

Da dumi-dumi: Tinubu ya fara fatali da manufofin Buhari

“An kama waɗanda ake zargin kuma sun amsa laifukan da ake zargin su da aikatawa,” in ji runudnar.

Wadannan sune wadanda ake zargi

Ta ƙara da cewa da ma Ugwu ya saba yi wa mata masu ciki “allurar da ke kaiwa ga rasa rayukansu”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...