Kansilolin Bunkure da Wata Gidauniyar Kiwon Lafiya Sun Karrama Ministar Abuja Dr. Mariya

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Karamar ministar babban birnin tarayya Abuja Dr.Mariya Mahmoud Bunkure Takarbi Lambar yabo matsayin gwarzuwar mace mai kishin Al’ummah da cigaba daga kansilolin Karamar hukumar Bunkure.

Kansilolin sun ce sun Karrama ministar ne saboda irin gagarumar da take bayarwa wajen tallafawa al’umma a Karamar hukumar Bunkure da yankin Rano Kibiya da Bunkure da ma jihar kano baki daya ba.

Talla

Lambar yabon da zababbun kansilolin karamar hukumar Bunkure suka Shirya mata kuma suka mika mata ta hannun babban mataimaki a gareta SA. Hon. Abba Kawu Gurjiya ta Isa Gareta a jiya talata.

Hukumar Tace Fina-Fina ta Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Zargin da ake yiwa Jaruma Maryam Yahya

Sai kuma lambar yabon da wata Gidauniyar kiwon lafiya ta bata mai suna AMBIENCE OF HOPE EXEPTIONAL FOUNDATION ta hannun babban mai taimaka mata na musamman SA. Abdullahi Isah Kauranmata.

A lokuta daban-daban ministar ta sami lambobin yabo daga kungiyoyin daban-daban, saboda irin gudunnawa da jajircewa da take yi wajen taimakawa masu karamin karfi a cikin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...