Hukumar Hisbah ta Kano ta kama mota maƙare da kwalaben giya dubu 24

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wata babbar mota makare da kwalaben barasa sama da 24,000.

Babban daraktan hukumar ta Hisbah ta jihar Kano, Abba Sufi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na hukumar, Lawan Ibrahim Fagge a yau Laraba a Kano.

Talla

Hukumar, wacce ta yi kamen a hanyar Zariya a Kano, ta kuma kama direban motar da wasu mutane biyu.

Da dumi-dumi: Tinubu ya fara fatali da manufofin Buhari

“Motar da ke dauke da kwalabe daban-daban na barasa sama da 24,000 an kwace daga hannun masu fasa kwaurinta a hanyar Zariya da tsakar dare.

“Jami’an Hisbah a jihar sun himmatu wajen aiwatar da manufar ba-sani-ba-sabo ga fasakwaurin barasa da sauran abubuwa masu sa maye a cikin jihar,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...