Da dumi-dumi: Tinubu ya fara fatali da manufofin Buhari

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta rufe asusun ajiyar kudi na kasa wato (TSA) da gwamnatin Muhammadu Buhari ta yi amfani da shi wajen tara kudaden shiga.

Sai dai gwamnatin tarayya ta umurci dukkan ma’aikatu, da hukumomi da su tura kashi 100 na kudaden shiga zuwa asusun ajiyar kudaden shiga na yau da kullun, wani bangare na asusun tattara kudaden shiga (CRF).

Hukumar Tace Fina-Fina ta Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Zargin da ake yiwa Jaruma Maryam Yahya

CRF shine sabon asusu inda a yanzu gwamnatin Tinubu za ta karba tare da hada kudaden shigarta a cikin sa.

Talla

Hakan ya zo ne bisa wata takardar da mai kwanan watan 28 ga Disamba, 2023, wadda ma’aikatar kudi ta fitar a ranar Talata, 2 ga Janairu, 2024.

Wannan umarni dai ya rufe asusun baitul mali na bai daya da tsohuwar gwamnatin Muhammadu Buhari ta yi amfani da shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...