Hukumar Tace Fina-Fina ta Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Zargin da ake yiwa Jaruma Maryam Yahya

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Hukumar tace fina-fina da daf’i ta jihar kano ta bayyana cewa ta wanke Jarumar masana’antar kannywood Maryam Yahaya bisa wani zargi da akai mata na rungumar wani saurayi a cikin wani bidiyo.

” An kawo mana korafi akan jaruma Maryam Yahaya kan wani bidiyo da ake yadawa a kafafen Sada Zumunta, Inda aka ga wani yana rungumar wata wacce ake zargin Maryam Yahaya ce, amma bayan mun gudanar da bincike mun gano cewa ba Maryam Yahaya ba ce a cikin bidiyon”.

Mai magana da yawun hukumar Abdullahi Sani Sulaiman ne ya bayyana hakan Yayin wata ganawa da yayi da freedom Radio dake kano.

Talla

Yace ban da aka Kai musu koken shugaban hukumar tace fina-fina ta jihar kano Abba El-Mustapha ya baiwa daraktan dake kula da Yan masana’antar kannywood damar gudanar da bincike don tabbatar da anyi adalci ga kowanne bangare.

 

” Bayan kammala binciken hukumar mu ta tabbatar da cewa Wacce ake zargin ba jaruma Maryam Yahaya ba ce, don haka muka ga dacewar mu fito mu shaidawa duniya cewa ba Maryam bace, saboda abun ya yadu da yawa bai dace mu yi shuru akan maganar ba”. Inji Abdullahi Sani Sulaiman

Gwamnan Kano Abba Kabir Ya Magantu Kan Batun Naushin Sakataren Gwamnati Baffa Bichi

Jami’in hulda da jama’a na hukumar ya bukaci al’ummar jihar kano da zu cigaba da baiwa hukumar hadin kai ta hanyar kai rahotannin abubunwan da suka ga ana yi a kannywood ba dai-dai ba, domin daukar matakin da ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...