Gwamnan Kano Abba Kabir Ya Magantu Kan Batun Naushin Sakataren Gwamnati Baffa Bichi

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya musa jita-jitar da ake yadawa na cewa sun yi dambe tsakaninsa da sakataren gwamnatin jihar Dr. Abdullahi Bappa Bichi.

Da yake jawabi yayin bikin rantsar da sabbin manyan sakatarorin gwamnati da masu ba da shawara na musamman a gidan gwamnati, Gwamnan ya bayyana cewa babu wani farfaganda da zai hana gwamnatinsa cimma burinta.

Talla

Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa nadin shugaban ma’aikatan jihar a matsayin mukaddashin SSG ba yana nufin an kori Baffa Bichi daga mukamin sa ba ne .

Yayin da yake magana kan yada labaran karya, Abba Kabir ya bayyana cewa, wadanda suke dauki siyasa a matsayin madogararsu ta rayuwa, su ne suke kirkiro jita-jita don tada hankulan da ba dole ba, amma kuma hakan su bai cimma ruwa ba .

Wakokin Kannywood 5 Da Suka Fi Shahara A 2023

Gwamna Yusuf, yace na bada rikon mukamin sakataren gwamnati ne saboda muhimmacin da mukamin yake da shi, ba zai yiwu a tafiyar da gwamnati a haka ba.

Gwamnan ya bada tabbacin idan Baffa Bichi ya samu sauki, to da zarar ya dawo zai cigaba da aikinsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...