Wani Magidanci da Iyalan sa sun yi Zanga-Zangar neman adalci ga kisan Masu Maulidi a Kaduna

Date:

Daga Aliyu Nasir Zangon aya

 

Wani Magidanci mai suna Aliyu tsoho Abdullahi mazaunin jihar Kaduna ya gudanar da zanga-zangar lumana tare da shi da ‘ya’yanshi da mai dakinsa, domin neman gwamnati ta dauki matakin hukunta Sojojin da suka sa bom a kan masu Maulidi a garin Tudun biri dake karamar hukumar igabi a jihar kaduna.

” Mun yi zanga-zangar ne mu biyar daga ni sai mai dakina da ‘ya’yana guda uku saboda da mu nunawa gwamnati cewa mun gaji da yadda ake kashe yan arewa babu gaira babu dalili da sunan kuskure Kuma a kasa hukunta wadanda sukai, don haka naje har helkwatar rundunar ƴan sandan jihar Kaduna domin mika koken mu”.

Talla

Da yake zantawa da wakilin kadaura24 a jihar Kaduna, Aliyu tsoho yace ya gamsu da irin tarbar da kwamishinan yan sandan jihar yayi masa , sannan ya bashi tabbacin jami’an tsaro zasu gudanar da cikakken bincike tare da hukunta duk wadanda aka samu da laifi a lamarin.

Kisan Masu Maulidi: Gwamnati ba da gaske take ba wajen yiwa musulmi adalci – Falakin Shinkafi

Da wakilinmu ya tambaye shi ko wadanne irin bukatu ya gabatarwa yan sanda? , Aliyu tsoho yace sun nemi a bayyana sakamakon binciken da za a yi, a hukunta masu hannu a kisan da neman biyan kuɗin diyyar rayukan wadancan bayin Allah da aka kashe ba tare da wani laifi ba.

” Na fadawa kwamishinan cewa idan har ba’a wadancan abun da na lissafa ba, wanda kuma shi duk mutanen arewa suka bukata to wallahi zan tara mutane mu tare hanyoyi mu Kuma hana duk wani aiki a jihar Kaduna har sai an yi mana abun da muke bukata” . A cewar Aliyu tsoho Abdullahi

Yace ya hana matarsa zuwa aiki sannan ya hana ya’yan su zuwa makaranta, duk don su nunawa duniya damuwarsu kan kisan da aka yiwa sama da mutane 127 wanda ko yan ta’adda basu taba yin irin shi ba. ” Amma abun mamaki jami’an da ya kamata su tsare mutane su kuma suke kashe su , babu shakka wannan abun taikaici ne.

Ga hotunan yadda Zanga-Zangar ta kasance

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...