Jam’iyyar APC zata lashe zaben gwamnan Kogi da rinjaye mai yawa – Ganduje

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Yayin da al’ummar jihar Kogi ke shirin gabatar da zaɓen gwamnan jihar a ranar 11 ga watan Nuwamba, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje, ya ce yana sa ran kashi 99 cikin 100 na goyon bayansu don samun nasara jam’iyyar a jihar.

 

Ganduje ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga mambobin jam’iyyar APC da magoya bayanta a wajen kaddamar da kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar a zaɓen ranar 11 ga watan Nuwamba.

Talla

Ya bayyana fatan al’ummar jihar za su kada kuri’arsu ga jam’iyya mai mulki domin jihar kogi dama jiha ce ta APC tuntuni, inji rahoton NAN.

Tinubu ya umarci jakadun Nigeria dukkanin su su koma Gida

“A yau muna kaddamar da kwamitin yakin neman zabe na jiha a hukumance wanda zai hada hannu da kwamitin yakin neman zabe na kasa da kuma kwamitocin yakin neman zabe na kananan hukumomi domin ganin mun sami nasara a zaben dake tafe”. Ganduje

 

“Kun ga irin kyakkyawan shugabancin da gwamnatin Gwamna Yahaya Bello ta yi muku, don haka a matsayinmu na jam’iyyar muke fatan za ku kara bamu dama don zabar dan takarar mu, Usman Ododo, domin yi muku aiyukan alkhairi .

Talla

Ododo danku ne, wanda kuka sani sosai a matsayin mutumin kirki mai aminci da aiki tukuru wanda a shirye yake hidimta muku da jihar kogi baki daya idan ya zama gwamna.

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya Nada Karin Manyan Mataimaka 57

“Ba mu sa ran samun nasara kasa da kashi 99 cikin 100 daga mutanen Kogi a zaben gwamnan da za a yi a ranar 11 ga watan Nuwamba,” in ji shi.

Ya shaida wa mazauna jihar cewa Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin samar da kyakyawan yanayin da ake bukata domin gudanar da zaben gwamna cikin lumana da aminci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...