Da dumi-dumi: Gwamnatin Kano ta rage kuɗin manya makarantu mallakinta

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

Gwamnatin jihar Kano, karkashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusuf, ta rage kaso hamsin cikin ɗari (50%) na kuɗin makarantun gaba da sakandare mallakin jihar.

 

” A Yau ( jiya litinin) na sami ganawa da shugabannin manyan makarantun gaba da sakandire na jihar kano, inda na umarce su da su rage kuɗin makarantun da kaso 50 ba tare da bata lokaci ba”. Inji Abba Gida-gida

Talla

Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan a sashihin shafin sa na Facebook jin kadan bayan kammala ganawa da shugabannin manyan makarantun .

Bai Kamata Gwamnatin Kano ta yi Auren Zawarawa a Wannan Lokacin ba – Shitu Sani Marshall

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito dalibai musamman wadanda suke Karatu a jami’o’in gwamnatin tarayya suna ta kokawa da yadda aka Kara Kudin makarantun.

Wannan mataki dai na gwamnatin jihar kano zai taimaka matuka wajen saukakawa dalibai su yi karatu cikin sauƙi a jihar kano.

Ko a makon jiya ma sai da gwamnatin jihar kaduna karkashin jagorancin Sanata Uba Sani ya bada tabbacin rage yawan kudaden manyan makarantun dake jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...