Ba daidai ba ne ki zama minista yayin da kike yiwa kasa hidima, NYSC ta fadawa ministar al’adu ta Nigeria

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na hukumar yi wa kasa hidima (NYSC), Eddy Megwa, ya bayyana cewa ministar fasaha da al’adu ta Nigeria, Hannatu Musawa, wadda a halin yanzu take yiwa kasa hidima na shekara guda, ta rike mukamin minista ba , haka ya sabawa  dokar NYSC.

 

Da take magana da wakilin Daily trust ta wayar tarho, Megwa ta tabbatar da cewa ministar yanzu haka ta shafe watanni takwas tana aikin yiwa kasa hidima a babban birnin tarayya Abuja.

Talla

Ya bayyana cewa ya sabawa dokar NYSC duk wani dan bautar kasa ya karbi duk wani mukami na gwamnati har sai ya kammala hidimar shekara daya.

Tinubu ya sake tura tawagar Malamai zuwa Jamhoriyyar Nijar

Ya ce tun a shekarar 2001 aka tura Hannatu Musawa sanana ‘yan yiwa kasa hidima dake jihar Ebonyi, amma daga baya ta koma jihar Kaduna domin ci gaba da shirin.

Ya ce lokacin da ta koma Kaduna ne ta gudu ba ta kammala shirin ba.

Hotunan yadda Sabon Shatale-talen Kofar Gidan Gwamnatin Kano ya kasance

Megwa ya ce hukumar NYSC zata duba batun ta kuma ɗauki matakin da ya dace akan Hannatu musawa .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...