Dr. Mariya Mahmoud Bunkure ta sake fito da darajar Kano yau a Abuja – Harazimi Rano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Dan gwagwaryar nan Kuma dan Siyasa Hon. Aliyu Harazimi Rano, yace abun da Sabuwar ministar Abuja Dr. Mariya Mahmoud Bunkure ta yi na kin baiwa shugaban kasa Tinubu hannu su gaisa ya sake fito da martabar jihar kano a idon duniya.

Talla

” Ka dubi alfarma irin ta Shugaban kasa wanda mutane da yawa sukan yi abun da bai dace ba don su faranta masa, amma a haka Mariya Bunkure ya Miko mata hannu su gaisa Amma taki bashi hannu saboda da tasan darajar kanta da Inda ta fito”.

Zanga-zanga haramun ce a addinin musulunci – Mal Dauda Lokon makera ya ƙalubalanci likitoci

Aliyu Harazimi Rano ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da jaridar kadaura24 a Kano.

Yace dama Mariya mace ce kamilallah wacce tasan mutuncin kansa da Inda ta fito, yace don haka tun da aka ayyana Sunanta a cikin jerin sunayen ministoci suke murna da farin ciki.

” Akwai da yawa matan aure da suke mantawa da aurensu da addinin su da Al’adar su su rika gaisawa da shugabanni, kaga ko tunda ita bata shita sahunta su ba, ai dole mu yaba mata Saboda mu Kara mata kwarin gwiwar cigaba da tsare mutuncin ta dana mutanen kano”. Inji Harazimi Rano

Hon. Aliyu Harazimi Rano wanda ya taba yin takarar shugabancin karamar hukumar Rano, ya ce suna da yaƙinin sabuwar Ministar garin abujan zata yi aiki tukuru don fitar da Ganduje da al’ummar jihar kano

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...