Ƙarin Kuɗin Jami’an: Majalisar Wakilan Nigeria ta Fadi Matsayarta

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Majalisar wakilan Nigeria ta bukaci hukumar kula da jami’o’i ta kasar (NUC) da ta dakatar da aiwatar da karin kudaden karatun jami’o’i.

 

Dan majalisar wakilai mai wakiltar karamar hukumar Dala daga Jihar kano Aliyu Sani Madaki (NNPP-Kano) ne ya gabatar da kudirin a zaman majalisar a ranar Talata.

Talla

Majiyar Kadaura24 Solacebase ta ruwaito cewa Madaki wanda ya bayyana cewa jami’o’in da suka kara kudadensu sun hada da Jami’ar Bayero ta Kano; Jami’ar Najeriya, Nsukka; Jami’ar Uyo; Jami’ar Maiduguri; Michael Okpara University of Agriculture, Umudike; da Jami’ar Tarayya da ke Dutse da dai sauransu.

Jerin sunayen ministoci: Shugaban APC, Adamu ya bayyana dalilin da ya sa Tinubu ya yi jinkiri fitar da ministoci

‘Yan majalisar yayin zaman nasu sun nuna damuwarsu kan yadda akai karin kudaden jami’o’in a dai-dai lokacin da al’umma suke cikin halin kakanikayi sakamakon talauci, hauhawar farashin kayayyaki, rashin aikin yi, da tashin farashin man fetur a baya-bayan nan.

‘Yan majalisar sun kuma yi nuni da cewa karin kudin jami’o’in na iya kara ta’azzara halin da kasar nan ke ciki, ganin cewa tuni dalibai suka fara yin barazanar da ka iya haifar da tada kayar baya ga Gwamnatin Tarayya, tare da haifar da mummunan sakamako ga kasar baki daya.

Majalisar ta kuma bukaci gwamnatin tarayya da ta janye karin kudin makaranta da aka yi a makarantun sakandare na kadaka wato Unity Secondary School.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...