Nada Haj. Amina HOD a matsayin kwamishina zai sake fito da kimar K/h Nasarawa – Matawallen Gwagwarwa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Tsohon dan takarar dan majalisar tarayya a karamar hukumar Nasarawa, Barr. Ibrahim Isa Aliyu, ya bayyana nadin da gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya yiwa Hajiya Aminu Abdullahi Sani a matsayin kwamishina da cewa an ajiye kwarya a gurbinta.

Talla

” Babu shakka gwamnan jihar kano yayi zurfin tunani da har ya dauko Hajiya Amina ya bata wannan mukami, Saboda tana da kwarewa da gogewa a fannin aikin gwamnati, sannan kuma ta bada gagarumar gudunmawa wajen tafiyar kwankwasiyya a Nigeria da jihar kano baki daya.

Da dumi-dumi: Kamfanin KEDCO ya bayyana dalilin da yasa za’a rasa wuta a Kano

Barr. Ibrahim Isa ya bayyana hakan ne lokacin da ya je taya Hajiya Amina Abdullahi Sani murna bisa wanann mukamin da ta samu.

Ya kamata ayi dokar da zata hana karya ka’idojin Hausa a allunan tallace – tallace – Dr. Saifullahi Dahiru

“Hajiya Amina dama can ta dauki dukkanin yan kwankwasiyya na karamar hukumar Nasarawa a matsayin ‘ya’yanta don haka Ina da kwarin gwiwar Hajiya zata taimaki yan kwankwasiyya sannan kuma ba zata baiwa gwamnan kano da jagoranmu na kwankwasiyya Kunya ba”. Inji Barr. Ibrahim Isa Aliyu

Barr. Ibrahim Isa wanda shi ne Matawallen Garin Gwagwarwa ya bukaci al’ummar karamar hukumar Nasarawa da jihar kano da su taya ta da addu’o’in samun nasara da kuma Allah ya bata ikon sauke nauyin da gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora mata.

Hajiya Amina Abdullahi Sani wadda akafi sani da Amina HOD tana cikin mutane ukun da gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya aikewa majalisar dokokin jihar kano sunayen su domin ta tantance su kuma ta amince masa ya nada su a matsayin kwamishinoninsa.

Tuni dai majalisar ta yi aikin da kundin tsarin mulkin Nigeria ya dora masu akan su , kuma har sun tantance su tare da amincewa gwamnan ya nada su a matsayin kwamishinoni .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...