Bidiyon Dala: Ganduje ya Magantu kan Gayyatar da Muhuyi Magaji Rimin Gado ya yi masa

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Tsohon gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ce har yanzu bai samu takardar gayyatar da ake cewa hukumar karɓar korafe-korafe ta jihar kano ta aika masa ba.

Tsohon kwamishinan yada labaran na tsohuwar gwamnatin Ganduje Kwamarat Muhammad Garba ne ya bayyana hakan ga sashin Hausa na BBC.

Talla

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa hukumar karɓar korafe-korafe da hana cin hanci da rashawa ta jihar kano ta ce ta gayyaci tsohon Gwamna domin ya bayyana a gabanta don amsa tambayoyi kan faifan bidiyon Dala da ake zargin Gandujen yana karɓar cin hanci daga wajen yan kwangila.

DA dumi-dumi: Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kano ta gayyaci Ganduje kan bidiyon Dala

Kuma dangane da sahihancin bidiyon da hukumar Muhyi take iƙirari, Muhd Garba ya ce ba za su ce uffan a kan wannan batu ba, don kuwa magana ce da take gaban kotu.

Umar Abdullahi Ganduje dai ya sha musanta zargin, inda ya riƙa iƙirarin cewa abokan adawa ne suka shirya maƙarƙashiya da nufin hana masa damar shiga zaɓen 2019.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...