Zargin Almundahana: Hukumar yaƙi da cin haci ta kama kwamishinan Ganduje da wasu mutane 5

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Hukumar karɓar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, ta kama tare da tsare kwamishinan ayyuka na tsohon gwamna Abdullahi Ganduje, Engr Idris Wada Saleh da wasu mutane biyar bisa zargin almundahanar Naira biliyan 1.

 

Majiyar Kadaura24, Solabase ta rawaito cewa an kama kwamishinan wanda kuma shi ne Manajan Darakta na Hukumar Kula da Titin Kano wato KARMA, da Babban Sakatare na Hukumar sayo kayiyyakin gwamnati, Mustapha Madaki Huguma, da Daraktan Kudi, sai kuma Daraktan Bincike da Tsare-tsare tare da wasu a ranar Litinin da yamma bisa zargin karkatar da sama da Naira biliyan 1 da aka yi wa kasafin gyaran wasu tituna guda 30 da magudanar ruwa a cikin birnin Kano .

Talla

Wata majiya a hukumar ta shaida wa Majiyar mu cewa an biya kudaden da aka cire a cikin asusun kamfanoni uku a ranar 25 ga Afrilu, 2023.

 

“Abin mamaki har hukumar sayowa da adana kayan gwamnati ta bayar da satifiket na rashin amincewa da kwangilar bayan an biya kudin kwanaki goma kafin ba da kwangilar, wanda hakan ya sabawa dokar sayan kaya ta jihar Kano ta 2021,” inji majiyar.

Sallah: Gwamnan Kano ya nemi afuwar Sarkin Gaya kan abun da ya faru a gidan gwamnati yau

“Kamfanonin na bogi suna dukkanin su suna da takardar rubutun wasiƙa guda ɗaya kuma ba tare da an San tartibin ofishin su ba.”

‘’Hukumar bin ka’idoji gwamnati ta ce ba a bayar da takardar shedar rashin amincewar ba, saboda hukumar kula da titinan Kano (KARMA) ta ce za a yi aikin gyaran hanyoyin ne ta hanyar aiki kai tsaye, amma takardun da aka basu suka karanta ba su nuna haka ba.

Kamfanonin sune North stone Construction Company Nig. Ltd, Arfat Multiresources Ltd da 1st Step Construction Ltd.

Kakakin hukumar Abba Kabir ya tabbatar wa majiyar mu cewa wadanda aka kama suna fuskantar tambayoyi kuma za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...