Gwamnatin Kano ta kafa kwamitin mutane 5 domin sake bude Makarantun kwana a jihar

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Umar Haruna Doguwa ya kafa wani kwamiti mai mutane 5 don shirin sake bude makarantun kwana da aka rufe a jihar.

 

Kwamishinan ya bayyana cewa a aiyukan da aka dorawa kwamitin ya zama dole yayi duba da muhimmancin da makarantu ke da shi a tsarin ilimin jihar.

Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na ma’aikatar ilimi ta jihar kano Aliyu Yusuf, ya aikowa kadaura24.

Sallah: Gwamnan Kano ya nemi afuwar Sarkin Gaya kan abun da ya faru a gidan gwamnati yau

Ya kara da cewa, za a binciki dalilin rufe wadannan makarantu da gwamnatin da ta shude ta yi da nufin gano hakikanin dalilan da suka sa aka dauki matakin, wanda ake dangantawa da matsalar tsaro.

Kwamishinan ya ce a cikin wasu abubuwa kwamitin zai fito da hujjoji kan dalilin da ya sa aka rufe makarantun a daidai lokacin da ake bukatar karin irinsu domin daukar daliban jihar.

NAHCON ta ayyana ranar da za’a fara dawo da Alhazan Nigeria gida

Ya kuma bayyana cewa, kwamitin zai kai rahoto ga ma’aikatar ilimi kan halin da makarantun suke ciki da yadda za’a farfado da su musamman ta fuskar kayan more rayuwa da sauran kayan aiki a makarantar.

Hon. Doguwa ya bukaci ‘yan kwamitin a lokacin da aka kaddamar da su da su yi aiki tukuru domin ganin an cimma manufar sake bude makarantun.

Ya jaddada cewa sabuwar gwamnatin jihar karkashin jagorancin Gwamna Engr. Abba Kabir Yusuf ta dukufa wajen ganin an ceto fannin ilimi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...