Bani da lokacin batawa wajen ramuwar gayya – Muhuyi Magaji Rimin Gado

Date:

Daga Nura Abubakar

 

Shugaban Hukumar karɓar korafe-korafe da hana cin hanci da rashawa ta jihar kano Barr. Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya ce ba zai tsaya duba abun da ya faru  bayan ya bar hukumar ba , kawai zai maida hankali ne waje ciyar da hukumar gaba da kuma kwatowa al’umma hakkinsu.

 

Muhuyi Magaji Rimin Gado ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa bayan rakiyar da yan uwa da abokan arzikin su sukai masa .

Tallah

Yace babu lokacin da zai tsaya yana rama abubuwan da akai masa a baya, duk da cewa yace bayan ya bar ofishin ya dawo ya iske an yi wata badakala, wadda kuma bazai bari ba saboda ba shi abun ya shafa ba.

Abba Gida-gida ya bayyana ma’aikatu ga sabbin kwamishinoni

” Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya bi umarnin kotu wajen dawo dani wannan matsayin don haka zan yi aiki tukuru don kara kare kambon wanann gidan na “Gatan mara Gata”. Inji Muhuyi

 

Shugaban hukumar karɓar korafe-korafe ta jihar kano, ya kara da cewa bayan dawowarsa hukumar ya fara bude wasu kararraki da aka shigar tun kafin tafiyar sa, amma yanzu ya fahimci akwai Almundahana da akai Inda aka nemi wasu matoci guda 7 da kuɗin ya akai Naira Miliyan 109 kuma ya rasa su.

Tallah

” Ina so ku sani akwai abubuwan da dagayyama akai yi su don idan mun fara bincike ace ramuwar gayya ce, ba mu da lokacin ramuwar gayya, amma fa hakan ba yana nufin zamu zuba idan a cutar da al’ummar jihar kano ba ne, kawai don kar ace mun yi ramuwar gayya”.

 

Ya bada tabbacin zai kara kyautata alakar aiki da ma’aikatan hukumar da sauran al’umma domin sauke nauyin da aka dora masa na mayarwa mai hakki hakkinsa. Sanann ya bada tabbacin Muhuyi Magajin da aka Sani shi ne ya dawo zai kuma yi aiki bisa doron dokokin hukumar karɓar korafe-korafe da hana cin hanci da rashawa ta jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...