Abba Gida-gida zai sake gina Alamar cikar Kano shekaru 50 da ya rushe a Na’ibawa

Date:

 

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada aniyarta na sake Gina sabon shataletale da ta rushe a hanyar shiga gidan gwamnati, zuwa hanyar kan titin gadar Sama dake Na’ibawa.

Bayanin Hakan ya fito ne daga gwamnan jihar Kano Engr.Abba Kabir Yusuf a yayin da ya ziyarci wurin da za’a sake ginin wanda suke tare da wadda ta yi zanan taswirar shataletalen kaltume Gana a Saban gurin da za a gudanar da wannan aiki.

” Sabon wurin da za’a sake gini dake nuna cikar Kano shekaru 50 ya ce sai yafi dacewa da wajen, kuma masana sun duba wajen sun tabbatar da cewa baza a sami wata matsala ba idan Akai gini a sabon wurin.

Tallah

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito gwamnatin jihar kano ta rushe shatale-talen dake Kofar gidan gwamnatin kano saboda dalilin tsaro da wasu dalilai da ta bayyana.

Hadiza Gabon ta Magantu kan batun kin auren Mutumin da ya kaita kara Kotu

A jawabinta wadda ta yi zanan taswirar ta ce hakika wajen ginin shataletalen ya dace zai Kuma kawatar da zarar an kammala aikin shi .

Ta Kuma godewa gwamnan jihar Kano bisa wannan dama da aka bata ta amfani da zanan taswirar da ta yi da jimawa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...