Yadda wani ma’aikacin wacin gadi ya tsinci kuɗin guzirin alhazan wata karamar hukuma a kano

Date:

 

Hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano ta bada tukuicin kujerar makka da takardar daukar aiki na dindin ga wani mutum da ya tsinci kuɗi har Naira miliyan goma sha shida a harabat hukumar .

 

Tun da fari dai mutumin mai suna Ɗangezawa ya bayyana wa majiyar kadaura24 Radio Kano cewa da misalin ƙarfe goma na daren ranar Alhamis ya tashi zai tafi gida sai ya ci karo da wata leda baƙa a daure, da ya duba sai ya ga Dalar Amurka mai tarin yawa nan da nan hankalin sa ya tashi ya dauki ledar ya fasa tafiya gida, ya kwana a ofishin hukumar.

Zaben gwamnan kano: Inda aka Kwana game da karar APC da NNPP a Kotu

“Da gari ya waye sai na kaiwa shugaban hukumar Alhaji lamin Baba danbaffa shi ma hankalin sa ya tashi nan da nan aka bincika aka kuma tarar da ashe kudin guzurin maniyyatan ƙaramar hukumar birnin ne, nan take aka karbi wadancan kudade aka mika su ga jami’in kula da alhazzai na ƙaramar hukumar birnin”. Acewa Dangezawa

Kadaura24 dai ta gano Ɗangezawa ya shafe shekaru ashirin da daya yana aikin wuccin gadi ( casual) a hukumar, yanzu haka dai an bashi takardar aiki ta din-din (Permanent and Pensionable) an kuma yi masa alkawarin Kujerar aikin Hajji baɗi idan Allah ya kaimu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...