Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya musanta iƙirarin mawaƙin nan Femi Kuti ya yi a kansa, wanda ya ce Hukumar EFCC mai yaƙi da yi wa arziƙin ƙasa ta’annati ta gayyace shi kan zargin sha’anin kuɗi bayan wa’adinsa ya ƙare a matsayin mataimakin gwamnan Jihar Bayelsa.
A baya-bayan nan mawaƙin ya ce tsohon shugaban Najeriya ya taɓa zuwa EFCC a matsayin wanda aka yi wa tambayoyi ko gudanar da bincike a kan shi, sai dai wata sanarwa da tsohon shugaban ya fitar ta musanta hakan.
Gwamnatin Kano za ta rushe Masarautun Gaya, Rano, Bichi da Karaye da Kuma dawo da Sarki Sunusi
A ranar Juma’a ne Wealth Dickson Ominabo wanda jami’in yaɗa labarai ne a ofishin tsohon shugaban ƙasar ya fitar da sanarwar da ta ƙaryata wannan iƙirari.
Zabe Gwamnan Kano: Kotu ta amince da bukatar APC, na duba na’urar BVAS
Inda ya ce ya yi amfani da wasu bayanai da wasu suka riƙa yaɗa wa a baya kan shugaban domin su ɓata masa sunan, har suka riƙa cewa sai da ya je EFCC domin amsa tambayoyi.