Ɗalibai sun yi zanga-zanga kan garkuwa da ‘yan uwansu a Zamfara

Date:

 

Daliban Jami’ar tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zanga don nuna ɓacin ransu kan sace ‘yan uwansu ɗalibai da masu garkuwa da mutane suka yi a jihar.

 

Masu zanga-zangar sun fara taruwa ne tun daga Damba zuwa Sabon-Gida da ke makwabtaka ta jami’ar.

Kadan ya rage da na nada Aminu Ado a matsayin Sarkin Kano – Kwankwaso

Matafiya da dama ne suka maƙale a lokacin da fusatattun ɗaliban suka toshe babbar hanyar Gusau zuwa Funtua.

Duk da tarin jami’an tsaron da ke birnin Gusau, ɗaliban sun toshe babbar hanyar da ke haɗa jihar da jihohin Sokoto da Katsina da kuma jihar Kaduna.

Tallah

Daliban sun ce a ranar juma’a da daddare masu garkuwa da mutanen sun sace ‘yan uwansu ɗalibai a garin Damba da ke wajen birnin Gusau.

A ranar Litinin ne ake sa ran fara jarrabawa a jami’ar, to sai dai ɗaliban sun ce ba za su bari a fara jarrabawar ba, har sai an kuɓutar da ‘yan uwan nasu.

Jihar Zamfara na daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fama da matsalar masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...