Tirkashi! Hukumar EFCC ta gaiyaci ministocin Buhari guda 8

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Akalla ministoci takwas ne aka gayyata wadanda suka yi aiki a karkashin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari kan zargin cin hanci da rashawa, kamar yadda majiyar hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) ta bayyana.

 

Wasikun gayyatan dai, an bayyana cewa, sun bukaci tsofaffin manyan jami’an gwamnatin na Buhari da su je su yi bayanin yadda suka kashe kudaden da aka ware wa ma’aikatun su a wasu ayyukan da suka gudanar a lokacin da suke rike mukamansu.

 

Rahotanni sun nuna cewa an rubuta wasikun ne zuwa ga tsoffin ministocin kafin a dakatar da Abdulrasheed Bawa a matsayin shugaban hukumar.

Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya yi sabbin nade-naden mukamai

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta fara gudanar da bincike a kamar yadda wata Majiya dake cikin hukumar bayyana.

Kadan ya rage da na nada Aminu Ado a matsayin Sarkin Kano – Kwankwaso

Majiyar ta ce baya ga tsohuwar ministar harkokin mata, Pauline Tallen, wadda aka gayyace ta a makon da ya gabata bisa zargin almundahanar Naira biliyan 2 da kuma “bangaren kudaden da ake zargin an karkatar da su daga aikin wanzar da zaman lafiya na uwargidan shugaban kasar Afrika,” an kuma gayyaci wasu kusan guda bakwai.

Idan dai ba a manta ba a watan da ya gabata ne hukumar ta kama Sale Mamman, wanda kuma tsohon ministan wutar lantarki ne a zamanin mulkin tsohon shugaban kasa Buhari, tare da tsare shi bisa zargin almundahanar Naira biliyan 22 da ya shafi ayyukan wutar lantarki.

Hakazalika, an rawaito cewa tsohon ministan harkokin ‘yan sanda, Muhammad Maigari Dingyadi, shi ma an gayyaci shi kan yadda ake tafiyar da asusun ‘yan sanda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...