Tajudeen Abbas ya zama Shugaban majalisar wakilai ta 10

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

An zabi Tajudeen Abbas, dan majalisa mai wakiltar mazabar Zaria a matsayin shugaban majalisar wakilai ta 10.

 

Tajudeen Abbas ya samu kuri’u 353 inda ya doke abokan takararsa biyu Idris Ahmed Wase da Aminu Sani wanda ya samu kuri’u 3 kowanne.

 

Benjamin Kalu wanda ba shi da abokin hamayya , an bayyana shi a matsayin mataimakin kakakin majalisar.

 

Zababbun Mambobi dari uku da hamsin da tara ne suka kada kuri’a a yayin zaben shugabannin majalisr su biyu .

Abubuwan da ya kamata ku sani kan dokar ba wa ɗalibai bashin karatu a Najeriya

An dai gudanar da zaɓen ne ta hanyar kada hanyar kada kuri’a kamar yadda doka ta 10 ta Majalisar ta tsara.

Tsohon Shugaban masu rinjaye na majalisar, Alhassan Ado-Doguwa ne ya gabatar da kuɗirin zabar sabon kakakin wanda Nnolim Nnaji mai wakiltar mazabar tarayya ta Nkanu ta Gabas/Nkanu ta Yamma kuma ya amince da shi.

 

Bayan kammala kada kuri’a wanda ya dauki sama da awa daya, magatakarda na majalisar wakilai Yahaya Danzaria ya sanar da Tajudeen Abbas a matsayin Shugaban Majalisar ta 10

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...