‘Yan Kasuwar Kofar wambai sun Koka kan asarar da Rusan gwamnatin Kano ya ja musu

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

 

Gamayyar kungiyoyin kasuwar robobi ta kofar wambai ta koka dangane da matakin da gwamnatin jihar kano ta dauka na rushe gine-ginen dake filin idi, da kuma, yadda wasu batagarin matasa suke kwashe kayayyakin al’umma a matsayin ganima.

 

“Kamata yayi gwamnati ta yi duba na tsanaki da tausayawa yan kasuwa a matsayinta ta uwar kowa, da aka zabe ta domin ta yi fafutukar samarwa al’ummar jihar kano aiyukan yi don inganta rayuwar su”.

Da dumi-dumi: Bola Tinubu ya Magantu kan rushe gine-gine da gwamnatin Abba Gida-gida ke yi a Kano

Shugaban kungiyar Shariff Sama’ila na Ta’ala ne, ya yi koken lokacin da gamayyar kungiyoyin suka gudanar da taron manema labarai a kasuwar dake nan jihar kano.

 

Samaila Nata’ala, ya bayyana cewa, kananan ‘yan kasuwa da suka karbi hayar wuraren da take rusawa yanzu ta karya wasu da dama wadanda yanzu basu da tudun dafawa, sakamakon yadda aka hada da kayansu aka rushe da kuma wadanda bata gari suka kwasa da sunan ganima.

“Kamata yayi a rika baiwa mutane lokacin da za su rika kwashe kayayyansu domin kaucewa yin asarar da ba lallai ne su iya mayar da ita ba”. A cewar Sama’ila Nata’ala

Shugaban gamayyar kungiyoyin ya jaddada cewa, kungiyoyin a shirye suke idan gwamnatin jihar kano ta nemesu su zauna domin tattaunawa kan yadda za’a shawo kan matsalar dake tsakanin gwamnati da al’ummar da suka mallakin gurare a yankunan.

Haka zalika, yace kungiyoyin masu biyayya ne ga tsarin gwamnati, amma akwai bukatar yin duba na musamman akan lamarin nasu duba da asarar da sukai waccce har yanzu ba su kai ga tantance ta ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...