Hotuna: Wasu matasa sun farwa sabbin shagunan tsohuwar Triumph dake Fagge

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Rahotanni daga karamar hukumar Fagge da ke jihar Kano na nuni da cewa wasu matasa sun kewaye tsohon ginin kamfanin jaridar Triumph inda aka gina rukunin shaguna na zamani masu hawa uku suna kokarin kwashe kayayyakin dake ciki.

wasu ganau sun tabbatarwa kadaura24 cewa masu kwangilar aikin sun shiga ciki da mota domin kwashe wasu kayayyaki bayan wasika da ake zargin an rubuta kan rushe ginin.

 

Duk da cewa an girke Jami’an tsaro a kofar shiga, matasan sun balle kofar bayan ginin tare da fara cire kifofi da tagogi.

Ya zuwa yanzu dai matasan sun kwashe mafi yawa daga cikin kayan da aka Sanya a cikin gini duba da yadda matasan suka rika debo kaya irin su kofa tagogi, Kwanon rufi da ma rodikan da akai amfani da su wajen ginin .

KAYYASA! Hotunan yadda Abba Gida-gida ya rushe Daula otel da na Hajj Camp

Wannan dai na zuwa ne bayan da gwamnatin jihar kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta fara rushe wadansu gine-gine a jihar, Inda a yau Lahadi aka wayi gari da rushe ginin tsohuwar Daula Otel da  wasu gine-gene dake filin sansanin alhazai

Ga wasu daga cikin hotunan yadda matasan suka yi sabon ginin.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...