Za mu yo hayar motoci domin kwashe Sharar da ta cika titunan Kano – Abba Gida-gida

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya ba da umarnin a gaggauta kwashe Sharar da suka cushe wasu titunan birnin Kano.

 

Idan za’a iya tunawa gwamna Abba Gida-gida ya kafa wani kwamiti mai suna NAZAFA wanda ya haka da dukkanin masu ruwa da tsaki a harkar don magance matsalolin ambaliyar ruwa.

Hakan na cikin sanarwar da Sakataren yaɗa labaransa Malam Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aike wa kadaura24.

Bashin da Kwankwaso ya barwa Ganduje yafi wanda aka barwa Abba Gida-gida yawa – Musa Iliyasu Kwankwaso

Sanarwar ta ce taruwar Bola a kan tituna na nuna barazanar afkuwar ambaliyar ruwa.

 

“Ya zamar mana dole mu yo hayar motocin tifa domin kwashe tarin sharar da ake da ita a Kano , saboda hukumar REMASAB a yanzu bata da isassun motoci da kayan aikin da zata iya kwashe duk sharar da ake da ita a jihar kano”. Inji Abba Gida-gida

 

Sanarwar tace Gwamnan ya zargi tsohon gwamnan kano Ganduje da sayar da motocin kware shara da hukumar kware shara ta Kano take da su da sauran kayan aikin hukumar, Inda aka fake da hadin gwiwa da wani kamfanin yan kasuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...