Za mu yo hayar motoci domin kwashe Sharar da ta cika titunan Kano – Abba Gida-gida

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya ba da umarnin a gaggauta kwashe Sharar da suka cushe wasu titunan birnin Kano.

 

Idan za’a iya tunawa gwamna Abba Gida-gida ya kafa wani kwamiti mai suna NAZAFA wanda ya haka da dukkanin masu ruwa da tsaki a harkar don magance matsalolin ambaliyar ruwa.

Hakan na cikin sanarwar da Sakataren yaɗa labaransa Malam Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aike wa kadaura24.

Bashin da Kwankwaso ya barwa Ganduje yafi wanda aka barwa Abba Gida-gida yawa – Musa Iliyasu Kwankwaso

Sanarwar ta ce taruwar Bola a kan tituna na nuna barazanar afkuwar ambaliyar ruwa.

 

“Ya zamar mana dole mu yo hayar motocin tifa domin kwashe tarin sharar da ake da ita a Kano , saboda hukumar REMASAB a yanzu bata da isassun motoci da kayan aikin da zata iya kwashe duk sharar da ake da ita a jihar kano”. Inji Abba Gida-gida

 

Sanarwar tace Gwamnan ya zargi tsohon gwamnan kano Ganduje da sayar da motocin kware shara da hukumar kware shara ta Kano take da su da sauran kayan aikin hukumar, Inda aka fake da hadin gwiwa da wani kamfanin yan kasuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...