Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya Koka da yadda Ganduje ya bar masa bashi Mai tarin yawa

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Sabon Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya Koka da yadda tsohon gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje ya bar masa bashin da yakai sama da Naira Biliyan 241 .

” Wanann abun da tsohuwar gwamnati ta yi mana abun takaici ne na bar masa bashin da yakai Sama da Naira Biliyan 241, a Ina za mu samu wadannan kudaden har mu biya”. Inji Abba Kabir

Sabon gwamnan ya bayyana hakan ne jim kadan bayan ya karɓi ragamar mulkin jihar Kano a Gidan gwamnatin Kano.

Abba Kabir Yusuf ya bada tabbacin zai duba yadda gwamnatin tada gabata ta gudanar da mulkin da kuma daukar matakan da suka dace.

” Na zaci tsohon gwamna Ganduje zai tsaya da kansa ya mika mulki kamar tadda aka Saba a nan kano, a Shekarar 1999 Kwankwaso ya mila mulki ga Kwankwaso, Kwankwaso kuma ya mika mulki ga Shekarau a 2003 , haka kuma Shekarau ya mikawa Kwankwaso mulki a Shekarar 2011, shi ma Kwankwaso ya mikawa Ganduje Kwankwaso mulkin a Shekarar 2015 , amma kuma ni Mai yasa ba zai tsaya ya mikamin mulki ba sai dai ya sa wakili ? “. Inji Abba Gida-gida

Engr. Abba Kabir Yusuf ya baiwa al’ummar jihar kano tabbacin gwamnatin sa zata yi duk mai yiyuwa wajen ganin bai basu Kunya ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...