Abba Gida-gida ya bayyana kadarorinsa kwanaki kadan Kafin karɓar mulki

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Gwamnan Kano mai jiran gado Abba Kabir Yusuf ya ayyana kaɗarorin da ya mallaka ga hukumar ɗa’ar ma’aikata.

 

Sanarwar da ofishin gwamnan mai jiran gado ya fitar a ranar Juma’a ta ce Abba Kabir Yusuf ya gabatar da kansa ga ofishin hukumar ɗa’ar ma’aikata da ke Kano tare da miƙa fom da ya cike na ƙadarorinsa.

 

“Na cika sharuɗɗan da kundin tsarin mulki ya gindaya na ayyana ƙadarorin da na mallaka kafin rantsar da ni a 29 ga Mayu,” in ji sanarwar.

Gobara ta tashi a Gidan da Ganduje ya Koma makonni biyu da suka gabata

Abba Kabir Yusuf ya kuma sanar da matakin a shafinsa na Twitter

Gwamnan mai jiran gado ya kuma bayyana cewa dukkanin jami’an da za su yi aiki a gwamnatinsa da suka ƙunshi har da muƙaman siyasa sai sun bayyana ƙadarorinsu kamar yadda doka ta tanada.

A ranar Litinin 29 ga Mayu za a rantsar da Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin sabon gwamnan Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...