KAYYASA! : Awanni kadan kafin saukarsa, Ganduje ya Rantsar da Sabon kwamishina

Date:

Daga Kabiru Yusuf

Awanni kadan kafin ya sauka gwamnan jihar Kano mai barin gado Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya rantsar da sabon kwamishina a hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar kano KANSEC.

 

Kwamishinan shari’a na jihar Kano Barr. M A Lawan ne ya rantsar da sabon kwamishinan mai suna Abdullah Abba Sumaila, yayin taron majalisar zartarwar jiha na ƙarshe wanda ya gudana daren jiya a gidan gwamnatin kano.

 

Da yake jawabi bayan rantsar da sabon kwamishinan gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya ce an rantsar da kwamishinan ne bayan majalisar dokokin jihar kano ta tantance tare da Amincewa da nada shi a matsayin kwamishina.

 

” Muna fata zaka yi aikin ka yadda ya dace saboda muhimmancin da hukumar zabe take da shi musamman wajen shirya zaben kananan hukumomi a jihar kano”.

 

An dai rantsar da sabon kwamishinan ne awanni kasa da 48 a rantsar da sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar kano Engr. Abba Kabir Yusuf.

 

Sai dai mukamin kwamishina irin wannan na wannan hukumar ba kamar sauran kwamishinoni na siyasa da aka Sani ba , domin shi wa’adi ne da shi na kamar yadda doka ta gindaya .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...